Advertisment
EducationNews

Asuu Zata Janye Da Yajin Aikin Da Tadade Tanayi

Sponsored Links

Shugaban kungiyar mallaman Jami’o’in nigeria Asuu farfesa victor Emmanuel osodeke yace Nan ba dadewa ba zasu koma bakin aikin koyarwar da suke Yi
Ya bayyana hakan ne yayin da ya gana da kakakin majalissar wakilan nigeria, femi Gbajabiamila a ranar litinin

Farfesa osodeke ya yabawa matakin da majalissar wakilan kasar ta dauka na tsoma Baki domin anyi sulhu tsakanin gwamnatin da kuma kungiyar mallaman Jami’o’in wato Asuu
Wacce ta kwashe wata takwas tana yajin aikin

Wani bidiyo da aka wallafa a shafin tuwita na majalissar wakilan nigeria ya nuna farfesa osodeke Yana cewa sun kusa kawo karshen yajin aikin

Wanda zuwa yanzu dai tuni labarin saura kiriss asuu ta janye yajin aiki ya watsu a kafafan yada labarai sosai

Ana sa ran dai asuu zata janye yajin aikin da ta Dade tanayi Nan da kwana biyu

Sponsored Links

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button