Advertisment
News

Sunayen ‘Yan Alfarma da Aka Tura Hukumar ‘Yan Sanda Domin Samun Aiki

Sponsored Links

Rundunar ‘Yan Sanda Najeriya ta fara aikawa ‘yan alfarma saƙonnin tes (SMS) na jerin sunayen Supplementary List. Sun fara aikawa da saƙonnin ta wayarsu domin sanar da su sunayen wadanda aka yi wa hanya ta musamman.

Yanayin Aikin

Wannan jerin sunaye na ‘yan siyasa ne, wadanda suka samu damar shiga jerin sunayen bayan sun kammala gwaje-gwajen lafiya. ‘Yan siyasa ne suka amshi sunayen mutane daga bayan an gama gwaje-gwajen lafiya suka tura su ga hukumar ‘yan sandan.

Kiran Hukumar ‘Yan Sanda

Hukumar ‘yan sandan Najeriya ta gayyace su a cikin jerin Supplementary List zuwa yin gwaje-gwajen lafiya. Amma a cikin jerin sunayen farko da aka saki, babu wanda aka yi wa hanya ta musamman ta hanyar ‘yan siyasa.

Tsarin Daukar Ma’aikata

Gwamnatin tarayya ta tsara cewa za a dauki mutane 10 daga kowanne daga cikin kananan hukumomi 774 na kasar. Wannan ya sa aka dauki mutane 7,740 daga jerin sunayen farko.

Alfarma da ‘Yan Siyasa

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar da umarni a dauki mutane dubu goma aiki a cikin rundunar ‘yan sandan Najeriya. Wannan ya sa aka bai wa ‘yan siyasa, sanatoci, ‘yan majalisan wakilai, da manyan sarakuna wasu alfarma domin daukar nasu mutanen.

Allah ya bamu sa’a.

Also Read: Dama ta Musamman Ga Masu Sha’awar Karatu a Kasar Saudiyya

Sponsored Links

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button