Advertisment
News

NPOWER TA SANAR DA ZATA SAKE DAUKAR MA’AIKATA MUTUM DUBU 400

Sponsored Links
Ministar harakokin Jinƙai da ci gaban Rayuwa ta ƙasa,
Sadiya Umar Faruk ta sanar da cewa gwamnatin taraiya na
shirin sake ɗaukar matasa dubu 400 a shirin N-Power.
Ministar ta yi sanarwar ne a Kano a jiya Laraba a gurin yaye
ƴan rukunin C1 na N-Knowledge a jihar Kano.
Ta ƙara da cewa adadin wani ɓangare ne na matasa miliyan
ɗaya da shugaban ƙasa ya sahale a ɗauka.
Ta ce matasa dubu 510 ne su ka amfana da shirin a rukunin
C 1, inda ta ƙara da cewa nan ba da daɗewa ba za a fara
rukunin C 2.
Sadiya ta yi bayani cewa shi shirin na N-Knowledge zai
taimakawa matasa ne wajen gogar da su kan harkar aikin
ofis, ƙirƙire-ƙirƙire da kuma harkokin kasuwanci a gida
Nijeriya da ma ƙasashen waje.
Ministar, wacce ta samu wakilcin Mataimakin Darakta a
ma’aikatar, Muhammad Sambo, ta ce matasa dubu uku ne
da ga yankin arewa-Maso-Yamma su ka samu horo kan
na’ura mai ƙwaƙwalwa a rukunin na C1.
Ta kuma yi kira ga matasan da su ka amfana da su yi ƙoƙari
su yi aiki da horon da su ka samu domin bunƙasa tattalin
arzikin su a rayuwa.
yanzu dai Haka mutane sun zuba Ido suna jiran sadiya Umar farouq ta sake daukan wasu na aikatan npower Bach c sauran ragowar da suka rage mutum dubu 400 
fatan sa a da nasara a rayuwar mu
Sponsored Links

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button