Advertisment
News

Ƙungiyar Masu Tuƙa A-Daidaita-Sahu a Kano Ta Janye Yajin Aiki

Sponsored Links

Ƙungiyar masu tuƙa baburan A-Daidaita-Sahu a Jihar Kano ta janye yajin aikin da take yi. Barrista Abba Hikima, lauyan da ke kare ƙungiyar, ya sanar da manema labarai matakin da ƙungiyar ta ɗauka na janye yajin aikin.

Tun a ranar Litinin, 10 ga watan Janairu, 2022 aka wayi gari da yajin aikin direbobin A-Daidaita-Sahu. An soma wannan yajin aikin bayan masu A-Daidaita-Sahun sun yi zargin cewa ana karbar musu kuɗaɗe na yin sabuwar lambar da suka yi rijista maimakon biyan kuɗin sabuntawa. Haka kuma, sun ce ana tatsar su sosai wajen karbar haraji daga naira 100 da suka saba biya, yanzu an mayar naira 120 a kowace rana. Sannan a cewarsu, sun nemi gwamnati ta ɗauke musu biyan harajin ranakun Lahadi tun da jami’an hukumar Karota ba sa fita aiki a ranar.

Sai dai gwamnatin Kano ta ce masu A-Daidaita-Sahun ba su da godiyar Allah.

Also Read: Dauda Kahuta Rarara Ya Bayar Da Motocin Da Za Ana Diban Jama a Kyauta A Kano

Sponsored Links

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button